Sudan: Kotu ta yanke wa shugaban rundunar RSF hukuncin kisa

Wata kotun Sudan, wacce ke yankin da sojoji ke iko da shi, ta yanke wa shugaban rundunar (RSF) da wasu sauran jami’an rundunar sojoji hukuncin

Wata kotun Sudan, wacce ke yankin da sojoji ke iko da shi, ta yanke wa shugaban rundunar (RSF) da wasu sauran jami’an rundunar sojoji hukuncin kisa a bayan idon sa saboda laifukan yaki a yammacin kasar, a cewar kafafen yada labarai na gwamnati.

Wannan ita ce hukunci na farko da aka yanke wa shugabannin RSF tun bayan fara yakin tsakanin wannan kungiyar sojoji da sojojin Sudan a watan Afrilun 2023.

Daga cikin mutane 16 da aka yanke wa hukuncin akwai shugaban RSF, Mohamed Hamdan Daglo, wanda aka fi sani da Hemedti, dan uwansa kuma mataimakin shugaban kungiyar, Abdelrahim Hamdan Daglo, da kuma wasu jami’an RSF da shugabannin kabilu daga Yammacin Darfur. Kotun da ke Port Sudan, wacce ke gabashin Sudan, ta same su da laifukan yaki, laifukan cin zarafin bil’adama, kisan kare dangi, da hare-hare kan fararen hula da kayayyakin more rayuwa na jama’a, in ji kamfanin dillancin labarai na kasar Sudan Suna.

Shari’ar ta mayar da hankali ne kan kisan gillar da aka yi wa gwamnan Yammacin Darfur Khamis Abakar a watan Yunin 2023, jim kadan bayan da RSF ta kama El-Geneina, babban birnin jihar. An kashe Abakar sa’o’i bayan ya zargi RSF da kawayenta da kai hare-hare kan fararen hula.

Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ta zargi RSF da kashe mutane har 15,000, galibi daga ƙabilar Massalit da ba Larabawa ba, a El-Geneina. Sojojin sun sha musanta aikata kisan kare dangi ko wasu laifukan yaƙi a Sudan.

Kotun Port Sudan ta sanar da cewa za ta tura shari’ar zuwa Kotun Koli don ƙarin nazari tare da neman a kama tare da mika waɗanda aka yanke wa hukunci, ciki har da ta Interpol.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted