Amurka ta kai hare-hare wa birane da dama a kudu maso yammacin Iran
Mataimakin Gwamnan Khuzestan kan harkokin Tsaro da Aiwatar da Dokoki ya bayyana cewa: “Tun daga safiyar Litinin, an kai hare-hare kan wurare da dama a biranen Ahwaz, Omidiyeh, Mahshahr, Behbahan, Dezful, Andimeshk, Abadan, da yankin Shadegan da makamai masu linzami na Amurka, kuma ana gudanar da bincike don tantance barnar da hare-haren ke iya janyowa.”
Waliyullah Hayati ya shaida wa manema labarai da safiyar Litinin cewa: “Tsakanin 1:35 zuwa 2:20 na safe, an kai hare-hare kan wurare da dama a biranen Ahwaz, Omidiyeh, Mahshahr, Behbahan, Dezful, Andimeshk, Abadan, da yankin Shadegan da makamai masu linzami na Amurka mai wuce gona da iri.”
Ya kara da cewa: “A Ahvaz, an kai hari kan wurare biyu a wajen birnin, kuma rahotannin cewa an kai hari kan filin jirgin sama ba gaskiya ba ne.”
Mataimakin Gwamnan Khuzestan ya ci gaba da cewa: “An kuma kai hari kan wani wuri a Andimeshk, wurare da dama a biranen Behbahan da Dezful, wurare huɗu a Omidiyeh da Mahshahr, da kuma wurare da dama a Abadan da yankin Shadegan.” Hayati ya ce: “Hukumomin da abin ya shafa suna tantance yiwuwar barnar da kuma duba yankunan da abin ya shafa, kuma za a bayar da ƙarin rahotanni bayan an kammala tantancewar farko.”