Ma’aikata goma na Jami’an Tsaron Cikin Gida na Siriya sun sami raunuka a lokacin rikicin da ya faru a yankin Suwaidan a kasar
An raunata ma’aikata goma na Jami’an Tsaron Cikin Gida na Siriya a lokacin arangamar da suka yi da ƙungiyoyin masu dauke da makamai na yankin a yammacin ƙauyen As-Suwayda, a kudancin Siriya.
Shafin labarai na gwamnatin Siriya, Al-Ikhbariya, ya ruwaito cewa: Jami’an sun ji raunuka ne yayin da dakarun gwamnati suka dakile hare-haren da ƙungiyoyi masu dauke da makamai suka kai kan wuraren bincike na tsaro kusa da ƙauyukan Al-Mansoura, Walgha, da Tell Hadid.
Majiya ta kuma ruwaito cewa: An kai hari kan ƙauyen Al-Mansoura da wani jirgin sama mara matuki ciki, wanda ya tabbatar da hasarar rayuka daga maharan, amma bai bayar da ƙarin bayani game da yanayin raunin da jami’an tsaro suka samu ba.