A ranar lahadi ce aka bude gasar cin kofin Afirka ta mata karo na 14 a Morocco inda mai masaukin baki ta shiga gasar da kafar dama bayan da ta doke tawagar Kenya da 4-0.
Tun a mintina na 30 da fara wasan Morocco ta zura kwallo uku a ragar Kenya sai kuma a minti na 32 yar wasan kasar Ibtissam Jraidi ta zura kwallo ta biyu a wannan karawa.
Tun da fari Aljeriya da Senegal suka kara a filin wasa na Moulay Souleimani inda Aljeriya ta doke Senegal da ci 2-0.
A jiya litinin rana ta biyu da soma gasar akwai wasa Afirka ta Kudu ta sha kashi a hannun Tanzaniya da ci 2-1 a wasan da suka buga a filin wasa na Moulay Rachid sai kuma wasa na biyu inda kasar Cote d’Ivoire ta doke Burkina Faso da ci 4-1 a wasan da suka buga a filin wasa na Larbi Zaouli da ke Casablanca.
A yau talata kuma najiriya za ta buda da Malawi sai kuma zanbiya ta kara da kasar masar.a gobe laraba kuma a kara tsakanin gana da cape verde sai kuma mali da kasar kamaru su kece raini