Wasu mutane masu dauke da makamai ne su ka kai hari da safiyar jiya Litinin a wani kauye da Jahar Kaduna wanda ya ci rayukan mutane 30.
Mazauna kauyen da lamarin ya faru sun sanar da yawan asarar raykan da aka yi, sannan kuma su ka kara da cewa da akwai kananan yara 8 a cikin wadanda su ka kashe din. Haka nan kuma sami wadanda su ka jikkata.
Yankin Arewa maso yammacin Nigeria da ya hada da Jahar Kaduna suna cikin inda aka fi samun tashe-tashen hankula na barayin daji da masu jabun jihadi.