Ministan kula da kiwon lafiya na kasar iran ya bayyana cewa kimanin mutane 60 ne suka yi shahada yayin da wasu guda 670 kuma suka jikkata sakamakon hare-haren da kasar Amurka ta kai a kudancin kasar a cikin kwanaki 10 zuwa 12 da ta sake kaddamar da yaki kan kasar
Kasar Amurka ta kaddamar da hare-hare a kasar iran a cikin kwanaki da suka gabata , inda suka mayar da hankali wajen kai hare-hare a yankunan dake kudancin kasar,kuma sun hari gadoji da wasu muhimman wurare na amfanin Alumma.
A matsayin matakin mayar da martani dakarun sojin kasar Iran sun kaddamar da hare-hare a sansanonin Amurka dake yankin, a kasashen tekun fasha da jodan, da kuma siriya, kuma sun kai hari kan muhimman wurare dake da alaka da kasar Amurka.
Wani da rahoto da kamfanin dillancin labarai na reuters nakalto ya nuna cewa mutum daya cikin mutane 3 a Amurka ne yake goyon bayan yakin da Trump ya kaddamar kan kasar Iran, inda mafiyawanci basa goyon bayan yakin da aka fara tun watanni biyar da suka gabata