Cibiyar Dakarun Sojin Amurk Ta Centcom Ta Sanar Da Kawo Karshen Sabon Harin Da ta Kaddamar  Kan kasar Iran

Rahotanni da kamfanin dillancin labarai na meher ya nakalto ya nuna cewa  cibiyar sojojin Amurka Centcom ta bayyana ce dakarun su sun  kawo karshen hare-haren

Rahotanni da kamfanin dillancin labarai na meher ya nakalto ya nuna cewa  cibiyar sojojin Amurka Centcom ta bayyana ce dakarun su sun  kawo karshen hare-haren da suka kai a kasar iran da misalin karfe 10 na dare agogon Amurka a jiya laraba, kuma sun ce sun kawo karshen mummunan harin da suka kai kan kasar iran cikin nasara

cibiyar sojin Amurka ta yi Ikirarin cewa a wannan harin sun samu gwamman wurare dake da alaka da dakarun kare juyin musulunci na iran da suka hada da cibiyar kwamandojin sojoji  da wuraren adana makami mai linzami da kuma jiragen sama marasa matuki da cibiyoyin sa ido a bakin teku da kuma dakarun sojin ruwan iran

haka zali acikin wannan bayani sun yi da’awar cewa babban manufarsu ta kai harin shi ne rage iran da kuma dakarun dake neman zama barazana ga sojojin Amurka  da jiragen ruwan kasuwanci  da kuma kasashen dake makwabtaka da gefe tekun farisa.

Centcom ta yi ikirarin cewa dakarun kare juyin musulunci na iran a ranar 28 ga watan yuli sun kadddamar da wani hari na ba zata da makamai mai linzami na ballistic a kan sansanin sojojin Amurka dake gabas ta tsakiya sai dai an harbo makaman da kuma lalatasu

kwamandan dakarun sojin Amurka daga karshe ya bayyana cewa sama da dakarun sojin Amurka guda dubu 50 ne da har yanzu suke gabas ta tsakiya kuma suna cikin shirin ko ta kwana.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted