Araqchi: Iran Tana Maraba Da Diflomasiyya Wajen Kare Al’ummarta

Ministan Harkokin Wajen Iran ya jaddada cewa: Suna maraba da hanyoyin diflomasiyya da ke tabbatar da haƙƙin al’ummar Iran Ministan harkokin wajen Iran ya gana

Ministan Harkokin Wajen Iran ya jaddada cewa: Suna maraba da hanyoyin diflomasiyya da ke tabbatar da haƙƙin al’ummar Iran

Ministan harkokin wajen Iran ya gana da takwaransa na China a birnin Beijing, inda suka tattauna dangantakar kasashen biyu da kuma ci gaban yankin.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi, wanda ya yi tafiya zuwa Beijing a matsayin jagoran tawagar diflomasiyya, ya gana da Wang Yi, memba na Ofishin Siyasa na Kwamitin Tsakiya na Jam’iyyar Kwaminis ta China kuma Ministan Harkokin Wajen kasar, kuma su biyun sun yi musayar ra’ayoyi.

A yayin taron, Araqchi ya lura da dadadden dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, inda ya bayyana China a matsayin abokiyar hulda ta kud da kud da Iran. Ya jaddada kudurin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na daukaka dangantakar dabaru da abokantaka a tsakanin Tehran da Beijing gaba daya a cikin tsarin hadin gwiwar dabaru tsakanin kasashen biyu, bisa girmama juna da kuma amincewa.

Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada muhimmancin dangantakar da ke tsakanin Tehran da Beijing, yana mai tabbatar da cewa wadannan dangantaka suna karkashin jagorancin shugabannin bangarorin biyu kuma bisa ga amincewar siyasa da ake da ita. Ya kara da cewa Tehran tana ba da muhimmanci musamman ga karfafawa da inganta dangantaka a fannoni daban-daban.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted