Wani Babban Malamin Addini A Lebanon Ya Ce Iran Ta Hana HKI Fadada Mamayar Kasashen Larabawa

Mataimakin majalisar koli da malaman shia a kasar Lebanon Sheikh Ali –Al-Khadib ya bayyana cewa, turjiya da kuma nasarar da JMI ta samu kan Amurka

Mataimakin majalisar koli da malaman shia a kasar Lebanon Sheikh Ali –Al-Khadib ya bayyana cewa, turjiya da kuma nasarar da JMI ta samu kan Amurka da HKI sun taimaka wajen dawo da zaman lafiya a yankin Asia.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Sheikh Ali Al-Khadib yana fadar haka a jiya Asabr, a taron manya manyan bakin JMI na Jana’izar Imam Shahid Khaminaei  anan Tehran.

Sheikh Khadib ya bayyana cewa, da Allah ya kiyaye, Iran bata sami nasara a wannan yakin ba, da kuwa HKI zata ci gaba da mamayar sauran kasashen larabawa makobtanta. Dangane da kasar Lebanon kuma Sheikh Al-Khadib ya godewa JMI dangane da taimakon da take bawa kungiyar hizbulla a fafatawar da take da HKI.

A ganawarsa da Aya. Reza Ramadani sakataren kungiyar Ahlulbaiti ta duniya Khadib y ace mutanen Lebanon sun yi hakuri sun kuma sha wahala a hannun yahudawa sahyoniyya amma shigowar kasar Iran ya taimaka wajen rage yawan matsalolin da yan shia a kasar Lebanon suke fuskanta.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted