Sudan Ta Yi Alkawarin Kare Hakkin Mahalarta Tattaunawar Kasa

Shugaban Majalisar Gudanar da Mulkin Soji a Sudan ya yi alƙawarin kare haƙƙin mahalarta tattaunawar kasa a Sudan Shugaban Majalisar Gudanar da Mulkin Sojin Sudan

Shugaban Majalisar Gudanar da Mulkin Soji a Sudan ya yi alƙawarin kare haƙƙin mahalarta tattaunawar kasa a Sudan

Shugaban Majalisar Gudanar da Mulkin Sojin Sudan kuma babban hafsan sojojin kasar, Abdel Fattah al-Burhan, ya sanar da cewa: Gwamnatin Kasar za ta samar da kariya ta wucin gadi da kuma garantin doka, siyasa, da tsaro ga mahalarta tattaunawar kasa da wata hukumar kasa mai zaman kanta ke jagoranta. Ya kuma bayyana cewa za a dakatar da shari’ar laifuka kan wadanda hukumomi suka shigar da kara a kansu.

A jawabin da ya gabatar da safiyar Asabar don tunawa da cika shekaru 72 da kafa rundunar sojin Sudan, al-Burhan ya ce wata kungiyar ‘yan kasar Sudan ta kasa ta fara wani shiri na tattaunawa ba tare da bata lokaci ba. Ya kara da cewa ya gana da mambobinta, ya saurari hangen nesansu, kuma ya amsa bukatunsu na samar da yanayi mai kyau ga tsarin siyasa.

Ya bayyana cewa kungiyar za ta yi aiki a matsayin wata hanya mai zaman kanta don gudanar da tattaunawar, tare da yin alkawarin samar da kariya ta wucin gadi da kuma garantin doka, siyasa, da tsaro ga mahalarta taron, baya ga samar da tallafin dabaru ga taron tattaunawar.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted