Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Ba za su durƙusa a gaban duk wani mai zalunci ba
Shugaban kasar Iran Mas’oud Pezeshkian ya jaddada cewa: Iran ba za ta taba mika wuya ga duk wani mai kai harin wuce gona da iri ba, yana mai cewa, “Za su tsaya tsayin daka a kan azzalumai har sai sun kai ga numfashi na ƙarshe, kuma za su mayar da martani da ta dace.”
Pezeshkian ya ƙara da cewa: Dole ne yaƙi ya ƙare a wani lokaci, yana mai cewa, “Ya fi dacewa a kawo ƙarshen yaƙin a yau, lokacin da suke kan kololuwar ƙarfinsu da mutuncinsu, kuma duniya baki ɗaya ta amince da nasarar Iran kuma ta amince da cewa Amurka ta kai hari kan makarantu, asibitoci, da kayayyakin more rayuwa a Iran wanda ya saɓa wa dokokin ƙasa da ƙasa, wani abu da duniya ke ƙyamata.”
Ya ci gaba da cewa, “A yau, sun yi imanin cewa dukkan shugabannin Iran da sojojin kasar a shirye suke su kare ƙasarsu.”
Pezeshkian ya jaddada cewa sakamakon tattaunawa babban nasara ne, wanda Majalisar Tsaron Ƙasa ta amince da shi tare da haɗin kai.