Jami’in Iran Ya Bayyana Dalilin Rashin Kai Hari Ta Kasa Kan Iran

Shugaban kwamitin tsaron ƙasa a majalisar dokokin Iran ya bayyana jigon dakile manufar maƙiya na kai hari kan Iran ta kasa tun farkon kaddamar da

Shugaban kwamitin tsaron ƙasa a majalisar dokokin Iran ya bayyana jigon dakile manufar maƙiya na kai hari kan Iran ta kasa tun farkon kaddamar da harin

Dangane da gazawar shirin makiya na kai hari kan Iran ta kasa, shugaban Kwamitin Tsaron Kasa da Manufofin Waje na Majalisar Dokokin Iran ya ce: “Ba zasu taba barin Amurka ba har sai ta sha kashi har zuwa karshen rikicin da ta kunna, kuma idan tsaron al’ummar Iran ya shiga cikin hatsari, to Iran za ta wurga tsaron makiya cikin mummunan hali a duk fadin duniya.”

Ibrahim Azizi ya bayyana haka ne a ranar Laraba a birnin Eqlid da ke lardin Fars a kudancin kasar, yana mai nuni da manufofi uku na makiya, wato mika wuya ga Iran, rusa ta, da kuma kawar da gwamnatinta – a lokacin yakin da aka yi sau biyu a baya. Ya jaddada cewa martanin Iran mai karfi da kuma wanda ba a yi tsammaninsa ba, ya tilasta wa abokin gaba amincewa da tsagaita bude wuta.

Dangane da yakin Ramadan da munanan laifukan da makiya suka aikata a cikinsa, ciki har da kisan gillar Jagoran juyin juya halin Musulunci da kuma harin makami mai linzami da aka kai wa makarantar Minab da birnin Lamard, ya kara da cewa: da mugun nufinsu, sun aiwatar da kisan gilla kan daliban Minab,  kuma sun aiwatar da kashe-kashen shugabannin Iran da kwamandojin sojojin kasar don tilasta wa Iran mika wuya da wannan matakan wuce gona da irin; Amma makircinsu ya gaza.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted