Hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 13 a kudancin Lebanon

Bayanai daga Lebanon na cewa hare-haren Isra’ila sun kashe akalla mutane 13 tare da raunata wasu 31 a wannan Talata a wani sabon saba wa

Bayanai daga Lebanon na cewa hare-haren Isra’ila sun kashe akalla mutane 13 tare da raunata wasu 31 a wannan Talata a wani sabon saba wa yarjejeniyar tsagaita wuta, kwana guda bayan da aka dakatar da sabon yaki tsakanin Isra’ila da Iran.

Wadanda aka kashe sun hada da wani namiji mai shekaru 16 wanda aka kashe a wani harin jirgin sama mara matuki a garin Haboush, a cewar kamfanin dillancin labarai na kasar Lebanon (NNA).

NNA ya ce wani harin Isra’ila a wani yanki na gidaje na jama’a a birnin Tyre ya kashe akalla mutane tara tare da raunata wasu 28.

An kuma kashe mutum daya a wani harin jiragen sama na Isra’ila a wata gona a garin Adshit a gundumar Nabatieh, in ji kamfanin dillancin labarai na kasar.

An kuma bayar da rahoton kai hare-haren sama a garuruwan Deir Qanoun, Ras al-Ain, al-Ramadiyah, da al-Abbasiyah da ke Tyre, amma har yanzu babu wani bayani game da raunukan da aka samu.

Jiragen sama marasa matuki na Isra’ila sun kai hare-hare sau biyu a jere cikin kasa da mintuna goma kusa da Husseini Club da ke garin Sharqiyah, inda suka raunata mutane uku, ciki har da mambobi biyu na Civil Defense na Lebanon.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted