Gaza: Mayaka Falasdinawa A Gaza Sun Wargaza Sansanin Sojojin HKI A Kusa Da Asbitin Shifa

Majiyoyin dakarun izzuddin Kassam da kuma Saraya Kudus a Gaza sun bayyana cewa mayakansu sun cilla makamai masu linzami wadanda suke cin karamin zango kan

Majiyoyin dakarun izzuddin Kassam da kuma Saraya Kudus a Gaza sun bayyana cewa mayakansu sun cilla makamai masu linzami wadanda suke cin karamin zango kan sansanin sojojin HKI a kusa da Asbitin Ashifa a yammacin Gaza, inda suka tarwatsa shi.

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto majiyan Saraya Kusdus ta kungiyar Jihadul Islami na bayyana cewa sun sami nasarar halaka sojan yahudawan sahyoniyya guda a gabacin birnin Gaza.

A wani labarin kuma jiragen yakin HKI sun yi ruwan wuta a sansanin yan gudun hijira da ke bakin ruwa a kusa da birnin Gaza inda Falasdinawa 2 suka yi shahada sannan wasu 10 suka ji rauni.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments