El-Rufa’i Ya Yargadi Ministan Tsaron Najeriya Kan kalaman Da Yayi

tsohon gwamnan kaduna ya ja kunnen ministan tsaron najeriya kan kalamansa na zargin da yake yi masa

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i ya bai wa Ministan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa mai ritaya wa’adin kwanaki 7 da ya gabatar da hujja kan zargin da ya yi masa na kitsa kashe-kashe a kudancin Kaduna ko kuma ya janye kalamansa.

Ministan ya zargi tsohon gwamnan da daukar matakan da suka raba kawunan al’umma tare da rura wutar matsalar tsaro a Kaduna a lokacin da yake rike da madafun ikon jihar tsakanin 2015 zuwa 2023.

A yayin wata hira da gidan talabijin na Channels cikin shirin ‘Politics Today’, ministan ya bayyana wa’adin mulkin El-Rufa’i a Kaduna a matsayin guda, yana mai cewa, mazauna yankin kudancin Kaduna ba su ji daɗin kashe-kashen da aka samu ba a yankinsu karkashin mulkin tsohon gwamnan

Ministan ya kuma zargin El-Rufa’i da bada umarnin rushe gidajen mutanen da yake da takaddama da su.

A wata Sanarwa ta samu sa-hannun Hon. Mohammed Bello El-Rufa’i, babban da ga tsohon gwamnan, ta kara da cewa, iyalansa sun damu matuka da kalaman da Musa yayin a hirar da kafar talabijin ta Channels tayi da shi a ranar 3 ga watan Satumba.

Sanarwar ta yi barazanar daukar matakin shari’a muddin wa’adin kwanaki bakwai ya kare ba tare da ministan ya janye kalamansa ba.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted