Yeman Ta Harba Wani Shu’umin Makami Mai Linzami Kan Isra’ila 

Yemen ta tabbatar da sake harba wabi makami mai linzami mai gudun tsiya kan Isra’ila. Da yake sanar da hakan Birgediya Janar Yahya Saree, kakakin

Yemen ta tabbatar da sake harba wabi makami mai linzami mai gudun tsiya kan Isra’ila.

Da yake sanar da hakan Birgediya Janar Yahya Saree, kakakin rundunar sojin kasar, ya sanar a wani jawabi da ya yi ta gidan talabijin yau Lahadi  cewa, bangaren dakarunsu na makamai masu linzami sun harba makami mai linzami samfarin Falasdinu-2 a tashar wutar lantarki ta Orot Rabin da ke Hadera, a yankin gabar tekun Mediterranean da Isra’ila ta mamaye.

Matakin ya cimma burin da ake so cikin nasara,” in ji Saree.

Ya kuma jaddada kudirin kasar Yemen na tallafawa Falasdinawa a Gaza, yana mai bayyana wannan aiki a matsayin wani bangare na “addini, da’a, da kuma hakkin bil adama na Yemen.”

Saree ya ci gaba da cewa matakin soji zai ci gaba da kasancewa muddin ana ci gaba da kai hare-hare kan Gaza.

Share

1 1 vote
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments