‘Yan Siriya Miliyan 1.1 Sun Rasa Matsugunni Bayan Kifar Da Mulkin Al-Assad

Hukumar kula da ayyukan jin kai ta Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa sama da mutane miliyan daya ne akasari mata da kananan yara ne

Hukumar kula da ayyukan jin kai ta Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa sama da mutane miliyan daya ne akasari mata da kananan yara ne suka rasa matsugunansu a Syria tun bayan da ‘yan tawaye suka kaddamar da farmaki a ranar 27 ga watan Nuwamba wanda ya kai ga kifar da gwamnatin Bashar Al-Assad a ranar Lahadi.

“Ya zuwa ranar 12 ga watan Disamba, mutane miliyan 1.1 ne suka rasa matsugunansu a fadin kasar tun bayan barkewar tashe-tashen hankula a ranar 27 ga watan Nuwamba.

“Mafi yawansu mata da yara ne,” in ji ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya OCHA a cikin wata sanarwa.

Kasar Siriya dai ta shiga rashin tabbas bayan da gungun ‘yan adawan dake dauke da makamai suka sanar da kifar da mulkin tsohon shugaban kasar Bashar Al-Assad.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments