Tashin Gobara A Kwale-Kwale Ya Lashe Rayukan Mutane 143 A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango

Bala’in Kogin Congo: Kwale-kwale ya kama wuta, ya kashe mutane 143 A wani mummunan lamari da ya afku a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, akalla mutane 143

Bala’in Kogin Congo: Kwale-kwale ya kama wuta, ya kashe mutane 143

A wani mummunan lamari da ya afku a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, akalla mutane 143 ne suka mutu, wasu da dama kuma suka bace bayan da wani kwale-kwale ya kama da wuta a kogin Kongo da ke arewa maso yammacin kasar.

Akalla mutane 143 ne suka mutu yayin da wasu da dama suka bace bayan da wani kwale-kwale ya kama da wuta a kogin Kongo da ke arewa maso yammacin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango, kamar yadda majiyoyin hukuma suka bayyana.

“An gano rukunin farko na gawarwakin mutane 131 a ranar Laraba, kuma an sake gano wasu 12 a ranakun Alhamis da Juma’a,” ‘yar majalisar wakilan kasar Josephine Pacific Lokomo ta shaida wa kafar yada labaran Faransa.

A nasa bangaren, Joseph Lokondo, shugaban kungiyoyin farar hula na yankin, ya bayar da bayanai kan adadin wadanda suka mutu na wucin gadi, wanda ya kai mutane 145.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments