Syria: Mutane Da Dama Sun Mutu Da Kuma Jikkata Sanadiyyar Gobara A Rumbun Ajiyar Makamai

An sami hatsarin tashin gobara a cikin wani rumbun ajiyar makamai a garin Mu’arrah dake gundumar Idlib ta Arewa, wanda ya yi sanadiyyar mutuwa da

An sami hatsarin tashin gobara a cikin wani rumbun ajiyar makamai a garin Mu’arrah dake gundumar Idlib ta Arewa, wanda ya yi sanadiyyar mutuwa da jikkatar mutane da dama.

Majiyar kiwon lafiya ta kasar Syria ta bayyana cewa; Mutane 2 sun rasa rayukansu, yayin da wasu 70 su ka jikkata sanadiyyar fashewar rumbun makamai a garin Mu’arrah Masrin.

Hukumar agjin gaggawa ta kasar Syria ta ce; Har yanzu babu cikakken dalili akan abinda ya haddasa wannan gobarar ta Mu’arrah Msarin.

Ma’aikatan kwana-kwana sun nufi wurin da gobarar ta tashi domin kashe wuta da kuma dauke mutanen da su ka jikkata.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments