Sudan ta soki shirun kasashen duniya game ta’asar dake faruwa a kasar

Ministan Harkokin Wajen Sudan Mohieldin Salem ya yi Allah wadai da shirun da kasashen duniya suka yi game da ci gaba da cin zarafin dan

Ministan Harkokin Wajen Sudan Mohieldin Salem ya yi Allah wadai da shirun da kasashen duniya suka yi game da ci gaba da cin zarafin dan Adam  da Rundunar Taimakon Gaggawa  ta (RSF) ke yi a yankunan El-Fasher, Darfur ta Arewa, da Bara, da Kordofan ta Arewa.

Ya yi wadannan kalaman ne a lokacin wani taro a Port Sudan da Darakta Janar na Kungiyar Kula da kaura ta Duniya (IOM), Amy Pope, wacce ta isa Sudan don ziyarar kwanaki biyar, a cewar kamfanin dillancin labarai na SUNA.

Salem ya yi Allah wadai da shirun da kasashen duniya suka yi game da ci gaba da take hakkin dan adam da RSF ke yi a El-Fasher da Bara.

Ya jaddada bukatar hada karfi da karfe na kasa da kasa don ayyana RSF a matsayin kungiyar ta’addanci.

 Ministan ya kuma sake jaddada cikakken kudurin gwamnati na samar da ayyukan jin kai da kuma tabbatar da tsaron ma’aikatan jin kai, yana mai nuna hadin gwiwa da ake ci gaba da yi da IOM, musamman a ayyukan da ke tallafawa komawar ‘yan gudun hijirar Sudan gida bisa rajin kansu.

Sudan na fuskantar mummunan rikicin jin kai sakamakon rikicin da ke tsakanin sojoji da RSF tun daga watan Afrilun 2023, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar dubban mutane tare da raba miliyoyi da gidajensu.

A ranar 26 ga Oktoba, RSF ta kwace iko da El-Fasher kuma ta yi kisan gilla a can, a cewar ƙungiyoyin cikin gida da na ƙasashen waje, duk da gargadin cewa harin zai iya ƙara ta’azzara rarrabuwar kawuna a ƙasar.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments