Sojojin Yemen Sun Sanar Da Kai Wa HKI Hare-hare Da Jirage Marasa Matuki

Kakakin sojojin Yemen Janar Yahya Sari ne ya sanar a jiya  Laraba da marece cewa; sojojin kasar sun kai wa hare-hare biyu da jiragen sama

Kakakin sojojin Yemen Janar Yahya Sari ne ya sanar a jiya  Laraba da marece cewa; sojojin kasar sun kai wa hare-hare biyu da jiragen sama marasa matuki zuwa yankunan Yafa da Asqalan dake HKI.

Janar Sari ya ce harin farkon dai sun kai shi ne akan wata cibiya mai muhimmanci a Yafa dake tsakiyar HKI,yayin da hari na biyu su kai kai shi a wani yanki na masana’antu dake Asqalan a kusa da Gaza.

Janar Sari, ya ce sun kai harin ne domin taimakawa Falasdinawa da ake zalunta, kuma  harin mataki ne na biyar a jerin hare-haren da suke kai wa HKI.

Kakakin na sojan Yemen ya kuma kara da cewa; Za su cigaba da kai wa HKI hare-haren har sai an kawo karshen yakin Gaza da kuma dauke wa yankin takunkumi.

Kusan kwanaki 4 kenan a jere da sojojin na Yemen suke kai hare-hare da jirage marasa matuki da  kuma makamai masu linzami akan muhimman cibiyoyin HKI.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments