Sojojin Ruwa na Kasar Iran Sun Fara Atisayi A Yankin Tekun Farisa

Babban kwamandan sojojin ruwa na JMI ya bada sanarwan cewa sojojinsa sun fara atisaiy daga farkon takun farisa har zuwa bakin mashigar ruwa ta Hurmus.

Babban kwamandan sojojin ruwa na JMI ya bada sanarwan cewa sojojinsa sun fara atisaiy daga farkon takun farisa har zuwa bakin mashigar ruwa ta Hurmus.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Alireza Tangsiri babban kwamandan sojojin ruwa na rundunar IRGC yana fadar haka a yau jumma’a. Ya kuma kara da cewa a shekarum baya rundunar sa ta sha yin atisayen hadin guiwa tare da wasu kasashen yankin da kuma wasu daga nesa a yankin don tabbatar da tsaron yankin don kuma musayar fasahar yaki tsakanin kasashen.

Tangsiri ya kara da cewa a wannan karon dan kadanne daga sojojin ruwa na rundunar IRGC ne suke gudanar da wannan atisayen.

Sannan ya bayyana manufar wannan atisayen a matsayin ta abota da zaman lafiya ga kasashe makobta sannan gargadi ga makiyan JMI.

Kwamandan ya kara da cewa rundunar a wannan atisayen zasu kaddamarda sabbin jiragen ruwa masu saurin da kuma makamai masu linzami daga gaba zuwa cikin teku.

Sojojin ruwa na rundunar IRGC zasu nuna korewansu a wannan atisayen inji shi.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments