Sojojin Isra’ila 825 Aka Kashe Tun Soma Yakin Gaza

Kafofin yada labaran Isra’ila sun ce akalla sojojin kasar 825 ne aka kashe a zirin Gaza tun a watan Oktoban da ya gabata. Kafofin yada

Kafofin yada labaran Isra’ila sun ce akalla sojojin kasar 825 ne aka kashe a zirin Gaza tun a watan Oktoban da ya gabata.

Kafofin yada labaran yahudawan sun kuma ce an kashe sojojin Isra’ila akalla 40 a birnin Jabalia da ke arewacin Gaza tun a watan da ya gabata, inda gwamnatin kasar ta tsananta hare-haren da take kai wa birnin.

A halin da ake ciki rahotanni sun ce an kashe sojojin Isra’ila akalla guda daya tare da jikkata wasu da dama bayan da mayakan Falasdinawa suka far wa sojojin a birnin Beit Hanoun da ke arewa maso gabashin birnin Gaza.

Wannan lamari dai na zuwa ne a daidai lokacin da yakin ya yi sanadin shahadar Falasdinawa kusan 45,550, galibinsu mata da kananan yara.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments