Rasha Da Amurka Sun Sake Dawo Da Gwaje-gwajen Makaman Nukiliya

Kasar Rasha ta sanar da samun nasarar gwajin jirgi maras matuki  na nukiliya wanda yake ninkaya a cikin ruwa. Gwajin dai ya biyo bayan wasu

Kasar Rasha ta sanar da samun nasarar gwajin jirgi maras matuki  na nukiliya wanda yake ninkaya a cikin ruwa.

Gwajin dai ya biyo bayan wasu gwaje-gwajen da Rashan ta yi ne na makamai masu linzami samfura mabanbanta masu iya daukar makaman  Nukiliya.

Jirgin  maras matuki mai daukar makamin Nukiliya  yana a karkashin rundunar sojan ruwan kasar,da aka bai wa sunan; Bosidon. Bugu da kari shi kanshi jirgin yana aiki ne da nukiliya a matsayin makamanshin da yake tafiyar da shi.

Shugaban kasar Rasha Vladmir ya ce; babu wata na’ura wacce za ta iya dakatar da wannan jirgin  mai ninkaya a cikin ruwa na Nukiliya.

Shugaban kasar ta Rasha ya kara da cewa; Wannan sabon makamin babu kwatankwacinsa a duniya saboda saurinsa da kuma nisan inda zai iya isa.

A gefe daya  shugaban kasar Amurka Donald Trump ya bai wa sojojin kasar umarnin sake bude gwaje-gwajen makaman Nukiliya.

Shugaban kasar ta Amurka Donald Trump ya rubuta a shafinsa na “Truth Social” cewa, ya bayar da umarnin sake dawo da gwaje-gwajen makaman Nukiliya.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments