Pezeshkian : Muna Fatan Yaki Da Zalinci Su Kawo Karshe A 2025

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana fatan cewa za a kawo karshen zalunci, tashin hankali, yaki, da kisan kare dangi a sabuwar shekara. A

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana fatan cewa za a kawo karshen zalunci, tashin hankali, yaki, da kisan kare dangi a sabuwar shekara.

A wani sako da ya aike a ranar Litinin, Pezeshkian ya mika gaisuwar Kirsimeti da sabuwar shekara ga shugabanni da al’ummar kasashen da ke murnar bukukuwan.

Ya bayyana fatan cewa za a samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya a shekarar 2025.

A wani sako na daban, Pezeshkian ya kuma taya shugabanni da al’ummar kasashen da ke murnar sabuwar shekara.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments