Ofishin Shugaban Iran: Ba a yanke shawara kan tattaunawa da Amurka ba

Mataimakin shugaban kasar Iran mai kula da harkokin sadarwa da yada labarai ya ce tafiyar da shugaban na Iran zai yi zuwa majalisar dinkin duniya

Mataimakin shugaban kasar Iran mai kula da harkokin sadarwa da yada labarai ya ce tafiyar da shugaban na Iran zai yi zuwa majalisar dinkin duniya za ta kasance a ranar 23 ga watan Satumba.

Mehdi Tabatabai, mataimakin mai kula da harkokin sadarwa da yada labarai a ofishin shugaban kasar Iran ya bayyana hakan ne a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Mehr, yayin da yake amsa tambaya game da yiwuwar yin shawarwari da Amurka a birnin New York, ya ce: “Na san dai akwai batun tafiyar, amma a halin yanzu babu wani batu na tattaunawa da Amurka a yayin wannan tafiya.”

Ya kara da cewa: “A cikin yanayi da halin da ake ciki  a yanzu, akwai bkatar taka tsantsan kan lamurra da dama.

Mataimakin shugaban kasar kan harkokin sadarwa da yada labarai ya kuma bayyana cewa: “A shekarar da ta gabata, yawan tarurruka da ganawa da shugaban kasar ya yi da shugabannin kasashe da tawagogin kasashen waje a Amurka ba a taba ganin irinta ba idan aka kwatanta da shekaru 14-15 da suka gabata.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments