Mutanen Gaza 18 Sun Yi Sahada A Cikin Sa’o’i 48

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinawa ta sanar da cewa an sami shahidai 12 da kuma wasu mutane da su ka jikkata sanadiyyar kisan kiyashi da

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinawa ta sanar da cewa an sami shahidai 12 da kuma wasu mutane da su ka jikkata sanadiyyar kisan kiyashi da sojojin mamaya su ka yi a wurare daban-daban.

Ma’aikatar kiwon lafiyar ta Falasdinawa ta sanar da cewa an kai gawawwakin shahidai 12 da kuma wadanda su ka jikkata su 41 zuwa asibitocin yankin a cikin sa’o’i 48 da su ka gabata.

Majiyar tashar talabijin din “Mayadin” ta ce, jirgin sama maras matuki na HKI ya kai hari  a kusa da shatale-talen al’manara dake gabashin birnin Gaza da hakan ya yi sanadiyyar shahadar mutane 4 da kuma jikkata wani adadi mai yawa.

Har ila yau wasu jiragen saman na ‘yan sahayoniya sun kai wani hari a unguwar “ Shuja’iyyah” da ya yi sanadiyyar shahadar mutane 6.

Bugu da kari wasu yankunan da hare-haren na ‘yan sahayoniya su ka shafa sun kunshi; unguwar “Sheikh Ridwan” dake arewa maso yammacin Gaza da unguwar “Karamah” .

Ya zuwa yanzu dai adadin wadanda su ka yi shahada a cikin shekara daya sun kai 45,553, yayin da wadanda su ka jikkata sun kai 108,379.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments