Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Isa Birnin Damascus Na Kasar Syria

Ministan harkokin wajen na jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakchi ya isa birnin Damascuss a yau Lahadi, a matsayin zangon farko na ziyarar da ya

Ministan harkokin wajen na jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakchi ya isa birnin Damascuss a yau Lahadi, a matsayin zangon farko na ziyarar da ya fara a cikin wannan yankin.

Ziyarar tasa a birnin Damascus tana nufin yin shawarwari akan yanayin da ake ciki a wannan yankin na yammacin Asiya, da kuma abubuwan da suke faruwa a cikin Syria.

Rahotannin farko da suke fitowa daga kasar Syria, sun ce an yi ganawa  a tsakanin Ministan harkokin wajen na Iran da Shugaba Basshar Asad na Syria.

 Gabanin barinsa Tehran ministan harkokin wajen na Iran ya bayyana cewa; Tabbas Iran tana goyon bayan gwamnatin Syria.

Har ila yau, Abbas Arakchi ya ce; Babu wani banbanci a tsakanin HKI da  ‘yan Takfiriyyah.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments