Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi

Jami’in kungiyar Hamas ya bayyana cewa: Kamen da hukumar Falasdinawa ta yi wa ‘yan gwagwarmaya a yankin Gabar Yammacin Kogin Jordan yana nuna goyon baya

Jami’in kungiyar Hamas ya bayyana cewa: Kamen da hukumar Falasdinawa ta yi wa ‘yan gwagwarmaya a yankin Gabar Yammacin Kogin Jordan yana nuna goyon baya ne ga ‘yan mamayar Isrta’ila

Jami’in kungiyar Hamas Abdel Rahman Shadid ya bayyana cewa: Kamen da jami’an tsaron Hukumar Falasdinawa suka yi na wani gungun ‘yan gwagwarmaya a Nablus da Jenin, da kwace makamansu, da kuma ci gaba da fatattakar ‘yan gwagwarmaya a duk fadin yankin gabar yammacin kogin Jordan, yana nuni da ci gaba da goyon bayan gwamnatin mamayar Isra’ila ce da murkushe al’ummar Falastinu.

A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, Shadid ya jaddada a cikin wata sanarwa da ya fitar cewa: Kamen da jami’an tsaron hukumar cin gashin kan Falasdinawa suka yi kan ‘yan gwagwarmaya da kuma fitattun al’umma da masanan Falasdinawa, biyan ladar moro-maron yahudawan sahayoniyya ne da jami’an hukumar Falasdinu suka ci.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ruguza gidajen mutane a Jenin, tare da koran dubban mutane a Tulkarm, ana kuma kwace yankunan mutane a gabar yammacin kogin Jordan.

Shadid ya bayyana cewa: Wadannan ayyuka suna nuna manufar Hukumar Cin gashin Falasdinawa ne na ganin ta raba ‘yan gwagwarmaya da yankin gabas yammacin kogin Jordan, tare da barin Falasdinu a bude ga sojojin mamayar Isra’ila gungun ‘yan ta’addan su aiwatar da tsare-tsaren Sanya Falasdinawa gudun hijira.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments