Kasar Rasha Ta Gindaya Sharadin Fara Zama Da Gwamnatin Amurka

Kasar Rasha ta sanar da sharadin komawa ga zaman tattaunawa da Amurka Ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov ya jaddada cewa: Farfado da kyakkyawar alaka

Kasar Rasha ta sanar da sharadin komawa ga zaman tattaunawa da Amurka

Ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov ya jaddada cewa: Farfado da kyakkyawar alaka tsakanin kasashen Rasha da Amurka ya dogara ne kan yadda Amurka ta kare masalaha da muradun Rasha.

Lavrov ya bayyana haka ne a yayin wani taron manema labarai cewa: “Idan bangaren Amurka ya kare muradu da masalahar kasar Rasha, to, tabbas tattaunawar da za a yi tsakanin kasashen biyu za ta farfado sannu a hankali, amma idan hakan bai faru ba, to al’amura za su ci gaba da kasancewa kamar yadda suke ba tare da canji ba.”

Lavrov ya yi nuni da cewa: Duk da cewa dangantaka za ta iya gyaruwa idan aka kare muradun Rasha, sai dai ba zai yiwu a yi tsammanin wani gagarumin sauyi mai kyau a dangantakar kasashen biyu ba a karkashin gwamnatin Shugaba Donald Trump na Amurka.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments