Kasar Jamus Ta Ba Da Shawarar Yadda Za A Gudanar Da Takunkumi Kan Kasar Siriya

Jamus ta ba da shawarar yin amfani da dabara mai kyau game da takunkumi kan Siriya Ministar harkokin wajen Jamus Annalena Baerbock ta bayyana cewa:

Jamus ta ba da shawarar yin amfani da dabara mai kyau game da takunkumi kan Siriya

Ministar harkokin wajen Jamus Annalena Baerbock ta bayyana cewa: “Jamus ta ba da shawarar yin amfani da dabara mai kyau da za a gudanar da takunkumin da aka kakabawa kasar Siriya, da haka zai Sanya al’ummar Siriya su samu saukin rayuwa.

Baerbock ta shaidawa manema labarai a birnin Riyadh na kasar Saudiyya a lokacin da take ganawa da ministocin harkokin wajen kasashen yammacin Turai da na larabawa a wani taron shiyya kan kasar Siriya da takwaransu na Siriya As’ad al -Shibani, tana cewa takunkuman da aka kakaba kan Siriya a lokacin shugabancin Bashar Asad kan laifukan tafka laifuka masu hatsari a lokacin yakin basasan kasar, dole ne a ci gaba da gudanar da takunkuman.

Ministar harkokin wajen kasar ta Jamus ta kara da cewa: “Yanzu haka al’ummar Siriya suna bukatar cin moriyarsu cikin gaggawa daga samun canjin Mulki a kasar, kuma kasashen Turai suna ci gaba da taimaka wa wadanda ba su da komai a Siriya, kamar yadda suka yi a tsawon shekarun a cikin yakin basasa a kasar, kuma kasashen Turai za su samar da karin kudi Yuro miliyan 50 na tallafin kayayyakin abinci, mafakar gaggawa da kuma kula da harkar kiwon lafiya.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments