Jamhuriyar Chadi Ta Sanar Da Soke Yarjejeniyar Hadin Gwiwar Tsaro Da Kasar Faransa

Ministan harkokin wajen kasar Chadi ya sanar da soke yarjejeniyar hadin gwiwa ta tsaro da kasar Faransa Rahotonni daga Chadi sun bayyana cewa: Jamhuriyar Chadi

Ministan harkokin wajen kasar Chadi ya sanar da soke yarjejeniyar hadin gwiwa ta tsaro da kasar Faransa

Rahotonni daga Chadi sun bayyana cewa: Jamhuriyar Chadi ta sanar da soke yarjejeniyar hadin gwiwa ta tsaro da kasar Faransa.

Ministan harkokin wajen kasar Chadi Abdur-Rahmane Kalamullah a ranar Alhamis da ta gabata ya sanar da cewa: Kasarsa ta soke yarjejeniyar hadin gwiwa ta tsaro da Faransa, sa’o’i kadan bayan ziyarar takwaran aikinsa na Faransa Jean-Noel Barrot a birnin N’Djamena fadar mulkin kasar ta Chadi.

Kalamullah a cikin wata sanarwa da ma’aikatarsa ​​ta wallafa a shafinta na Facebook, ya ce: Gwamnatin Jamhuriyar Chadi tana sanar da al’ummar Chadi da na kasa da kasa game da matakin da ta dauka na soke yarjejeniyar hadin gwiwar tsaro da aka kulla tsakaninta da Jamhuriyar Faransa.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments