Iran Za Ta Kaddamar Da Jirgin Kasa Mai Tsananin Sauri Tsakanin Tehran Da Mashhad

Babban darekta na zartar da manyan ayyuka na kamfanin jirgin kasa Ali Kazemi ya bayyana cewa za a  kaddamar  jirgin kasa mai matukar sauri a

Babban darekta na zartar da manyan ayyuka na kamfanin jirgin kasa Ali Kazemi ya bayyana cewa za a  kaddamar  jirgin kasa mai matukar sauri a tsakanin birnin Tehran zuwa birnin Mashahad a mako mai zuwa.

Darektan hukumar jiragen kasar na birnin Qum ya kara da cewa, idan aka shimfida hanyar wannan jirgin kasan mai hanzari za a rika isa Mashahd daga Tehran a cikin sa’oi 8 da mintuna 20 maimakon fiye da sa’aoi  12.

Kazemi ya kara da cewa, daya daga cikin muhimman manufofin jamhuriyar musulunci ta Iran shi ne hada hanyoyin kai da komowa a tsakanin muhimman biranen kasar da su ka hada da masu masana’antu.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments