Iran Ta Yi Watsi Da Zargin Faransa, Ta Ce Zargin Bai Da Tushe

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’il Baghae ya ti watsi da zargin kasar Faransa kan cewa It ace take son wargaza tsarin zaman lafiya

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’il Baghae ya ti watsi da zargin kasar Faransa kan cewa It ace take son wargaza tsarin zaman lafiya a yankin kudancin Asiya.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Baghaei yana fadar haka a nan Tehran, ya kuma kara da cewa, HKI ce abin zargim don nata laifuffukan sun sa kotun kasa da kasa ta fidda sammacin kama shuwagabanninta.

Amma kasar Iran yakamata a yabeta ne saboda kokarin da take yi na ganin zaman lafiya ta tabbata a kasashen yankin Asiya ta kudu.

Amma abin mamaki, shugaban Emmanuel Maocron na kasar Faransa, yana zargin kasar Iran da haddasa rikici a gabas ta tsakiya.

A wani bangaren, Macron ya zargi kasar Iran, dangane da shirinta na makamashin nukliya, inda Baqaie ya bayyana cewa, shirin nukliyar kasar Iran tana kan doka.  Ya ce a cikin wannan halin HKI tana kissan falasdiawa tana kuma, fadada kasarta a yankin gabasa ta tsakiya, amma Macron ya rufe idanunsa daga halin da ake ciki a Gaza a yayinda mafi yawan kasashen duniya suna allawadai.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments