Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta musanta zancen tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka kan cewa Iran ta amince ta takaita tashe mmakamashin Uranium kasa da kasha 1%.
Ta kuma bayyana cewa kasashen Turai basu isa su sake dawo da takunkuman tattalin arzikin na MDD a kan kasar Iran ba.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Ismail; Baghae yana fadar haka a jiya Litinin ya kuma kara da cewa. bukatar kasashen turai da sake dawoda takunkuman tattalin arzikin na MDD a kan Iran tare da amfani da tsarin sanapback na yarjeniyar JCPOA.