Iran Ta Bukaci Karin Taimako Daga MDD Don Kula Da Yan Gudun Hijiran Afganistan

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar a Iran ya gana da shugaban hukumar yan gudun hijira ta MDD, inda ya bukaci karin taimako daga hukumar don

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar a Iran ya gana da shugaban hukumar yan gudun hijira ta MDD, inda ya bukaci karin taimako daga hukumar don kula da miliyoyin yan gudun hijiran Afganisatn a kasar.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Seyed Mohammad Bathaei yana fadar haka a taron kwamitin gudanarwa na hukumar UNHCR karo na 76 a birnin Geneva na kasar Swizland.

Labarin ya kara da cewa Iran tana daga cikin kasashen da suke daukar bakwancin yan gudun hijira daga kasar Afganistan mafi girma a duniya. Rashin zaman lafiya a kasar Afganistan na shekaru fiye da 40 ya maida mutanen kasar da dama yan gudun hijira a kasashen duniya musamman kasashe makobta.

Filippo Grandi shugaban hukumar ta UNHCR ya yabawa kasar Iran a kokarin ta na kula da yan gudun hijiran Afganistan na lokaci mai tsawo  sannan ya yi alkawalin kara tallafi ga kasar.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments