Iran: Gharib Abadi Ya Ce Kada A Siyasantar Da Hukumar Hana Yaduwar Makaman Guba A Duniya

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan al-amuran sharia da kuma na kasa da kasa, Kazim Gharib Abadi ya bukaci hukumar yaki da hana amfani

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan al-amuran sharia da kuma na kasa da kasa, Kazim Gharib Abadi ya bukaci hukumar yaki da hana amfani da makaman guba a duniya kada ta shigar da siyasa a ayyukanta.

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto Gharib abadi yana fadar haka a wani jawabin da ya gabata  a jiya Litinin a taron hukumar ta CEC karo na 29 a birnin Haque na kasar Nethalands.

Ghariba Abadi ya kara da cewa matsayin JMI dangane da makaman guba a fili yake.

Ya kuma kara da cewa JMI itace kasa wacce tafi cutuwa da makaman guba a wannan zamanin, saboda yadda aka yi amfani da makaman guba a kan mutanen kasar Iran a yakin shekaru 8 da ta fafata da gwamnatin kasar Iraqi ta lokacin.

Mataimakin ministan ya yi kira ga kasashen yamma su dakatar da tallafin da suke bawa HKI a kissan kare dangin da take yi a gaza.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments