Hamas : Gazawar Isra’ila Ta Tilasta Mata Amincewa A Tsagaita Wuta

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta bayyana cewa gazawar Isra’ila wajen cimma burinta a Gaza ne ya tilasta mata amincewa a tsagaita wuta. Gazawar Isra’ila

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta bayyana cewa gazawar Isra’ila wajen cimma burinta a Gaza ne ya tilasta mata amincewa a tsagaita wuta.

Gazawar Isra’ila wajen cimma burinta ne ya tilasta mata sassauta ra’ayinta a teburin sulhu, a cewar Mohammad Nazzal, wani babban jami’i a fannin siyasa na kungiyar Hamas.

“Burin Isra’ila shi ne ta kubutar da mutanenta da aka yi garkuwa da su’’.

Babu daya daga cikin muradunta da ya biya,” in ji Nazzal a kebantacciyar tattaunawa da Anadolu Agency.

“Sun kasa yin amfani da karfin soji don kubutar da mutanensu da aka yi garkuwa da su don haka sai suka sassauta matsayinsu a lokacin tattaunawa.

A halin da ake ciki, babu yadda za a kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su idan ba ta hanyar sulhu ba,” a cewarsa.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments