Gaza : An Saki Falasdinawa 200 A Musayar Sojojin Isra’ila 4

Isra’ila ta ce ta saki Falasdinawa 200, ciki har da wasu kwamandojin kungiyar Hamas, a wani bangare na yarjejeniyar tsagaita bude wutar  da aka cimma

Isra’ila ta ce ta saki Falasdinawa 200, ciki har da wasu kwamandojin kungiyar Hamas, a wani bangare na yarjejeniyar tsagaita bude wutar  da aka cimma a Gaza.

Kungiyar kare hakkin fursunonin Falasdinu ta tabbatar da cewa daga cikin wadanda aka sako akwai Mohammed al-Tous, mai shekaru 69, wanda ya shafe kusan shekaru arba’in a tsare a hannun gwamnatin Isra’ila.

Musayar, wadda ita ce ta biyu tun bayan da tsagaitawar ta fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu, na zuwa ne bayan da Hamas ta saki wasu sojojin Isra’ila mata hudu a ranar Asabar.

Kungiyar agaji ta kasa da kasa ta Red Cross ta tabbatar da cewa a yanzu an kammala kashi na biyu na musayar fursunonin tsakanin Isra’ila da Hamas.

Isra’ila dai ta fitar da jerin sunayen fursunonin Falasdinawa sama da 700, wadanda za a saki a karkashin yarjejeniyar.

Fiye da fursunoni 230 ne ke zaman daurin rai da rai kuma za a tilasta musu gudun hijira na dindindin idan an sake su, ba wai dan su koma Falasdinu da zama ba saidai su nemi mafaka zuwa kasashen Aljeriya, Turkiyya ko Jordan a cewar kwamitin kula da harkokin fursunonin Falasdinawa dake da alaka da kungiyar kwantar ‘yancin palasdinawa ta PLO.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments