Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya yi Allah-wadai da matakin da Australia ta dauka na korar jakadan Tehran daga kasar saboda zarge-zargen da ake yi na kai hari kan wuraren yahudawa a cikin kasarta, yana mai bayyana hakan a matsayin wani shiryayyen aiki da ake nufin cimma wata manufa ta siyasa da shi.
A cikin wani rubutu a dandalin X ya rubuta cewa, “Iran na daya daga cikin tsofaffin al’ummomi na duniya, cikin al’ummar Iran har da yahudawa, saboda haka zargin Iran da kai hare-hare irin wadannan wuraren yahudawa Australia, yayin da muke basu kariya a cikin kasarmu zargi ne maras ma’ana,” in ji shi.
Araghchi ya kara da cewa, Iran na fuskantar wadanann zarge-zarge ne daga gwamnatin Australia saboda matsayarta a kan batun Falastinu, da kuma nuna Rashin amincewa da kisan kiyashin da Haramtacciyar Kasar Isra’ila ke yi a kan mata da kananan yara a Gaza.
A jiya Talata, Firayim Ministan Australia Anthony Albanese ya zargi Iran da kitsa hare-hare biyu kan wuraren Yahudawa a cikin watannin Oktoba da Disamba, zargin da aka yi ba tare da gabatar da wata hujja kan hakan ba.