Ministan harokokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya gana da tokwaransa na kasar Masar da kuma shugaban hukumar makamashin nukliya ta duniya Rafael Grossi a karon farko tun bayan yakin kwanaki 12 wanda kasashen Amurka da HKI suka kaiwa Iran a cikin watan yunin da ya gabata.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya bayyana cewa, Aragchi ya kai ziyarar aiki na kwana guda birnin Alkahira a yau Talata ce don tattauna batun shirin Nukliyar kasar Iran da shugaban hukumar IAEA Rafael Grossi a birnin Al-Khahira.
Labarin ya kara da cewa ministan ya ce Iran ta amince ta bude sabon shafi a huldarta da hukumar IAEA bisa wani sabon tsari wanda a cikin iran zata tabbatar da amincin shirinta na makamashin nukliya da kuma kare hakkinta na gasa makamashin uranium kamar yadda ya zo a cikin yarjeniyar NPT babu kare babu ragi.
Har’ila yau ana saran Aragchi zai gana da shugaban kasar Masar Abdulfatta Assi da kuma ministan harkokin wajen kasar a kebe, inda zasu tattauna. Dangantaka tsakanin kasashen biyu.