An Kashe Sojojin Mamaya A Gaza

Sojojin HKI sun sanar da cewa  an kashe biyu daga cikinsu a yakin da yake gudana a yankin Gaza A yau Talata ne dai sojojin

Sojojin HKI sun sanar da cewa  an kashe biyu daga cikinsu a yakin da yake gudana a yankin Gaza

A yau Talata ne dai sojojin mamayar  su ka sanar da cewa, biyu daga cikin jami’ansu na soja sun halaka a fadan da ake yi a Gaza, daya daga cikinsu mai suna Itan Yisra’il Shiknai dan shekaru 24, wanda mataimakin kwamandan bataliya ta 932 ne. Shi kuwa na biyun day a halaka sunashi Dapir Tision Rifah dan shakaru 28, kwamanda ne na rundunar Nahal.

Wannan dai yana zuwa ne a daidai lokacin da yakin na Gaza yake cika shekaru 459, kuma sojojin mamaya suke cigaba da kai hare-hare akan Falasdinawa.

A jiya Litinin kadai Falasdinawa 22 ne su ka yi shahada,yayinda ake cigaba da fada a tsakanin ‘yan mamaya da ‘yan gwgawarmaya a Gaza.

A can yammacin kogin Jordan ma Falasdinawa guda biyu sun yi shahada sanadiyyar harbinsu da sojojin mamaya su ka yi a garuruwan Nablus da Tubas.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments