An Dawo Da Zirga-zirgar Jirage Kai Tsaye Tsakanin Iran Da Saudiyya

Bayan tsaiko na tsawon shekaru 9, an dawo da zirga-zirgar jiragen saman a tsakanin Iran da Saudiyya, inda wani jirgi daga Mashhad ya tashi, ya

Bayan tsaiko na tsawon shekaru 9, an dawo da zirga-zirgar jiragen saman a tsakanin Iran da Saudiyya, inda wani jirgi daga Mashhad ya tashi, ya sauka a Dammam a gabashin Saudiyya.

Wadanda su ka halarci saukar jirgin na kamfanin “ Homa” na Jamhuriyar musulinci ta Iran a can kasar Saudiyya sun hada da jakadan Iran a Riyadh, sai kuma wakilan hukumar jiragen sama ta kasar Saudiyya.

Ofishin jakadancin jamhuriyar musulunci ta Iran dake Riyahd ya sanar da cewa daga yanzu an bude Zirga-zirgar jiragen sama a tsakanin kasashen biyu, bayan da  cibiyoyin sufuri na kasashen su ka dauki dukkanin matakan da su ka dace na ganin hakan ta faru.

Ma’aikatar sufuri ta sanar da cewa; A yau Talata ne aka dawo da zirga-zirgar jiragen saman a tsakanin Mashahad zuwa Dammam wacce kamfanin jirgin sama na “ Homa” na Iran ya bude. Bugu da kari a kowane mako a ranakun  Talata da Alhamis jirgin zai rika zuwa Saudiyya.

Birnin Dammam yana a gabashin Saudiyya ne kuma shi ne cibiyar gundumar gabashin kasar da take a gabar ruwan tekun Pasha.

Share

5 1 vote
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments