Al Burhan : ‘Yan Mulkin-mallaka’ Ne Ke Rura Fituna A Afirka

Shugaban majalisar mulkin sojin kasar Sudan Janar Abdel Fattah al Burhan ya bayyana cewa ‘yan mulkin-mallaka ne suke kara rura wutar duk wani rikici a

Shugaban majalisar mulkin sojin kasar Sudan Janar Abdel Fattah al Burhan ya bayyana cewa ‘yan mulkin-mallaka ne suke kara rura wutar duk wani rikici a Afirka.

Al Burhan ya bayyana haka ne a yayin ganawarsa da shugaban kasar Guinea Bissau Umaro Sissoco Embalo a Bissau.

Al Burhan da Embalo sun gudanar da wani taron koli na kasashen biyu da zummar tattaunawa kan batutuwan da suka shafi kasashen da kuma hanyoyin inganta hadin-gwiwa.

Janar Al’Burhan ya ce a halin da ake ciki yanzu, Afirka ta farka, kuma hakan ya ba da damar yin adawa da tsoma bakin kasashen waje a harkokin da suka shafi nahiyar.  

Muna yaba kokarin wasu kasashen Afirka, wadanda suka yi tsayin daka wajen adawa da mulkin-mallaka zamanin baya da na yanzu.”

A ranar Lahadi ne dai shugaba Al Burhan ya isa kasar Guinea-Bissau, kasa ta biyu a rangadin da yake yi a Afirka, wanda ya fara daga Mali a ranar Asabar kana ana sa rai zai je Saliyo da Senegal a nan gaba.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments