Yemen: Amurka Da Birtaniya Sun Kai Wa Kasar Yemen Hare-hare

Rahotanni da suke fitowa daga kasar Yemen sun ce, jiragen yakin Amurka da na Birtaniya sun kai hare-hare akan gundumar Hudaidah dake gabar ruwan tekun

Rahotanni da suke fitowa daga kasar Yemen sun ce, jiragen yakin Amurka da na Birtaniya sun kai hare-hare akan gundumar Hudaidah dake gabar ruwan tekun “Red Sea” a yammacin Yemen.

Wannan harin dai yana zuwa ne  saboda matsawa San’aa ta dakatar da hare-haren da sojoji suke cigaba da kai wa manufofin HKI a karkashin taimakawa Gaza.

Jagoran kungiyar “Ansarullah” ta Yemen Abdulmalik Al-Husi ya sha nanata cewa ba za su daina kai irin wadannan hare-haren ba komai girman matsin lambar da za a yi musu, har sai in an kawo karshen yakin Gaza.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments