Trump Ya Yi Barazanar Korar Daliban Da Ke Goyon Bayan Falasdinawa

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar rage kudaden da gwamnatin tarayya ke ba wa kwalejoji da jami’o’in da ke ba da izinin ” zanga-zangar

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar rage kudaden da gwamnatin tarayya ke ba wa kwalejoji da jami’o’in da ke ba da izinin ” zanga-zangar goyan bayan Falasdinawa tare da hukunta daliban da suka shiga irin wannan zanga zanga.

Trump ya yi wannan gargadin ne a wani sako da ya wallafa a dandalinsa na sada zumunta bayan da masu zanga-zangar goyon bayan Falasdinawa suka taru a harabar jami’ar Columbia da ke New York.

Shugaban na Amurka ya kara da cewa “za a daure masu tayar da hankali” ko dai a daure su ko kuma a tura su dindindin zuwa kasashensu na asali.”

Ko da yake bai ambaci musamman zanga-zangar goyon bayan Falasdinawa a cikin sakon nasa ba, amma a baya Trump ya yi barazanar korar duk daliban da suka shiga zanga-zangar adawa da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi wa Falasdinawa a zirin Gaza.

A karshen watan Janairu, Trump ya rattaba hannu kan wata doka da ta bukaci gwamnati ta kori daliban kasashen waje da suka shiga zanga-zangar goyon bayan Falasdinu.

Ya yi zargin cewa zanga-zangar da aka yi a harabar jami’ar ta haifar da “kyama, barna da kuma cin zarafi a kan ‘yan kasarmu, musamman a makarantunmu da harabar jami’armu.”

Kungiyoyin kare hakkin bil’adama da masana shari’a sun dage cewa wannan umarni ya saba wa ‘yancin fadin albarkacin baki da kundin tsarin mulkin kasar ya tanada.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments