Sojoji Sun Sanar Da Kwace Mulki A Kasar  Guinea Bissau

Rahotanni sun bayyana cewa wasu masu dauke da makamai sun kama shugaban kasar Guinea Bissau Umaro Sissoco Embalo a yau Laraba, kwanaki uku bayan da

Rahotanni sun bayyana cewa wasu masu dauke da makamai sun kama shugaban kasar Guinea Bissau Umaro Sissoco Embalo a yau Laraba, kwanaki uku bayan da aka yi zaben shugaban kasa.

Rahotannin sun ce an yi ta harbe harbe a babban birnin kasar, a yayin da Alummar kasar ke zaman jiran sakamako zagaye na farko na zaben shugaban kasa da aka yi a ranar Lahadi.

Zuwa yanzu ba a tabbatar da ko su wane ne suka yi harbin ba.

Rahotannin sun kuma ce an yi ta harbe harben a kusa da fadar shugaban kasar da ofishin hukumar zabe a yau Laraba, inda mutane suka tarwatse suna neman mafaka.

A jiya Talata ne dai shugaban mai ci Umaro Sissoco Embalo, da babban abokin hamayyarsa Fernando Dias, suka yi ta ikirarin yin nasara a zaben wanda ya kamata a yi tun a shekarar da ta gabata.

Guinea Bissau dai ta fuskanci juyin mulki har karo hudu da rashin zaman lafiya tun bayan samun ƴancin kai daga Portugal a 1974.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments