SADC Zata Ci Gaba Da Wanzar Da Dakarunta A Gabacin Congo Duk Tare Da Nasarorin Da M23 Take Samu

Shuwagabannin kungiyar kasashen raya tattalin arziki da kuma tsaron kasashen Afrika da kudu ta ce zasu ci gaba da wanzar da sojojinsu a kasar Congo

Shuwagabannin kungiyar kasashen raya tattalin arziki da kuma tsaron kasashen Afrika da kudu ta ce zasu ci gaba da wanzar da sojojinsu a kasar Congo duk tare da sauye-sauyen da kungiyar yan tawaye na M23 suka yi a yankin arewacin KIVU.

Shafin yanar gizo na Labarai ‘Africa News” ya bayyana cewa shuwagabannin kungiyar sun bada wannan sanarwan ne bayan wani taron gaggawa da suka gudanar a kasar Zibabwe a ranar Jumma’an da ta gabata.

Shugaban kungiyar na riko-riko kuma shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, ya yim kira ga kungiyar ta kasance mai nuna karfi da da kuma juriya kan abubuwanda da ke faruwa a arewacin congo.

Sojojin tabbatar da zaman lafiya na kungiyar a cikin makonnin da suka gabata sun fuskanci koma baya a hannun sojojin M23, inda suka kashe sojojin kungiyar kimani dozen guda daga kasashen na SADC.

Affirka ta kudu, Malawi, da Tanzania sun rasa sojoji a dai dai lokacinda sojojin M23 suka shiga birnin Goma babban birnin. A halin yanzu dai shugaba Tsetsekedi ya fara tattara sojojin kasar don kare birnin Kinshasa babban birnin kasar ta Congo.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments