Ministan harkokin wajen kasar Nijar ya sanar da cewa nan ba da jimawa ba za a Rasha za ta aika tawagar diflomasiyya a Nijar.
Nijar ta tabbatar da aniyar ta na karbar bakuncin ofishin jakadancin Rasha a karon farko cikin sama da shekaru talatin, in ji ministan harkokin wajen kasar ta yammacin Afirka, Bakari Yaou Sangare a ranar Alhamis.
Bayanin ya fito ne yayin wani taron manema labarai na hadin gwiwa a birnin Moscow bayan tattaunawa tsakanin ministan harkokin wajen Rasha Sergey Lavrov da takwarorinsa na kasashen Nijar, Mali, da Burkina Faso.
M. Sangare ya bayyana cewa, a halin yanzu Nijar na neman wurin da ya dace domin gina ofishin jakadanci na tawagar diflomasiyyar Rasha a kasar, ya kara da cewa Yamai na fatan nan ba da jimawa ba Moscow za ta nada jakada.
‘’Mun rufe ofishin jakadancinmu a Rasha a cikin 1990s, amma daga baya mun gane cewa wannan kuskure ne,” in ji shi.
Lavrov ya tabbatar da cewa kasashen biyu suna kan hanyar dawo da wakilcin diflomasiyya. “A nan gaba kadan, tare da taimakon ku, za mu kammala dukkan ayyukan don dawo da ofishin jakadancinmu.
Kuma tabbas za mu yi hakan a cikin shekarar nan ta 2025,” in ji ministan harkokin wajen Rasha.
A farkon wannan shekara, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha Maria Zakharova ta tabbatar da cewa, Moscow na da niyyar bude sabbin ofisoshin jakadanci a kasashen Afirka da dama da suka hada da Nijar, Saliyo, da Sudan ta Kudu.