Palasdinu: Sojojin “Isra’ila” 3 Su Ka Jikkata Sanadiyyar  Taka Su Da Mota

Rahotanni daga Ramallah sun ce a kalla sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila 3 ne su ka jikkata sanadiyyar  taka su da mota da wani Bapalasdine ya

Rahotanni daga Ramallah sun ce a kalla sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila 3 ne su ka jikkata sanadiyyar  taka su da mota da wani Bapalasdine ya yi , a yau Talata.

Kafafen watsa labarun “Isra’ila” sun ambaci cewa; Wani Bafalasdine ya soka wa dan shayoniya wuka da aka dauke shi zuwa asibiti domin karbar magani.”

Majiyar ta ce da akwai sojojin a wurin da aka kai hari, don haka su ka bude wuta akan maharin Bapalasdine.”

Su kuwa jaridun Falasdinawa a Ramallah sun ce wanda ya kai harin na Yau Talata ya yi shahada bayan da sojojin mamaya su ka bude masa wuta.

A gefe daya, kungiyoyin gwgawarmayar Falasdinawa sun yi maraba da harin  akan ‘yan sahayoniya a kusa da Ramallah, tare da bayyana shi a matsayin mayar da martani ga laifukan yakin da suke tafkawa akan al’ummar Falasdinu.

Kungiyar Hamas da ta fitar da bayani ta yi jinjina akan ci gaban gwagwarmaya a yammacin kogin Jordan, duk da matsin lamba da takurawar da sojojin mamaya suke yi.

Haka kuma ta ce; jinanen shahidai za su ci gaba da zama masu karfafa gwiwar mutane domin ci gaba da yin gwgawarmaya.

Ita ma kungiyar Jihadul-Islami ta bayyana harin da cewa, Na jarunta ne’ kuma mayar da martani ne akan laifukan ‘yan mamaya.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments